Mai Martaba Sarkin Mutane Masu Bukata ta Musamman Alhaji Shehu Umar yabayya jindadinshi ga Gwamna Lawal Kan Kafa Hukumar Masubukata Tamusamman A Zamfara
Daga Aliyu Buhari Gusau
Sarkin Masubukata ta Musamman, Alhaji Shehu ya yabawa gwamnatin jihar Zamfara kan kafa hukumar Masu bukata ta Musamman a jihar.
Sarkin ya yi wannan yabon ne a fadarsa dake Gusau babban birnin jihar.
Alhaji Shehu ya nuna farin cikinsa na kafa hukumar, ya bukaci gwamnatin jiha data aiwatar da hukumar, “Yanzu muna da Darakta Admin da Daraktan Kudi a Hukumar”
"Kamar yadda muka sani an kirkiri hukumar ne domin Masubukata ta Musamman, yakamata yazama sunyi zasufi anfana,” inji sarkin.
Ya yabawa dan majalisar jiha mai wakiltar Zurmi ta gabas, Hon. Salihu Usman Zurmi nakai korafin kafa hukumar a majalisar dokokin jihar.
Ya bada tabbacin cigaba da ba gwannati hadinkai da goyon baya nagani tacigaba.
Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da sucigaba da addu’ar zaman lafiya da kwanciyar hankali, duba da cewa babu wata al’umma da zatacigaba ba tare da zaman lafiya ba.
Comments
Post a Comment